Ofishin MDD a Afrika ta kudu ya tabbatar a ranar Litinin cewa, an tsinci gawar wani jami'in MDD a wani tsauni na Table Mountain dake birnin Cape Town, jami'in ya bace ne tun a watan Maris.
Charlotte Nikoi, daraktan kula da ma'aikata na hedkwatar ofishin tallafawa kananan yara na MDD (UNICEF) a birnin New York, ya bace ne a watan Maris a lokacin da yake hutu tare da iyalansa a Cape Town.
Dama dai 'yan sanda sun kaddamar da binciken neman Nikoi, amma ba su same shi ba. A makon jiya, 'yan sanda suka tsinci gawarsa a tsaunin Table Mountain. Bayan wasu gwaje gwaje da aka yi kan gawar, an gano cewar Nikoi ne, dan shekaru 50 da haihuwa dan asalin kasar Ghana.(Ahmad Fagam)