in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNHCR ta kadu da mutuwar 'yan gudun hijura a dajin sahara
2017-06-03 12:19:23 cri
Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD UNHCR ta bayyana cewa, ta kadu matuka da samun labarin mutuwar a kalla 'yan gudu hijira da bakin haure kimanin 44 a cikin rairayin Sahara a wannan makon, galibinsu daga kasashen Najeriya da Ghana.

Mai magana da yawun babban sakataren MDD Farhan Haq ya shaidawa taron manema labarai a jiya Jumma'a cewa, wadanda suka tsira sun ba da labarin cewa, motar da mutane 50 din dake ciki a kan hanyarsu ta zuwa Libya ne ta lalace tsakanin biranen Agadez da Dirkou dake hamadar Saharar a yankin arewacin Jamhuriyar Nijar, lamarin da ya cusa su cikin tsananin zafi da karancin ruwan sha, kuma mutane shida ne kadai suka tsira.

Hukumar ta UNHCR ta sake yin kira ga kasashen duniya da su dauki matakan da suka dace don magance yadda jama'a ke kokarin kaura zuwa kasashen waje. Yanzu haka hukumar tana neman taimakon dala miliyan 75.5 don kara agazawa harkokin jin kai da biyan bukatun jama'a a kasar Libya, ciki har da wadanda suka bar muhallansu da masu karbar bakuncinsu gami da 'yan gudun hijira da masu neman mafaka. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China