in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 6 sun mutu sakamakon lamuran tsaro guda uku a London
2017-06-04 17:23:04 cri
Bangaren 'yan sadan kasar Burtaniya a jiya Asabar ya ce, a daren ranar an samu abkuwar lamuran tsaro guda uku a birnin London, ciki har da wata babbar mota mai daukar kaya ta ci karo da mutanen dake tafiya a gadar Landan, wanda ya haddasa rasuwar mutane 6.

Bangaren 'yan sandan London ya bayar da sanarwa cewa, yanzu 'yan sandan suna bincike kan lamarun uku da suka faru a gadar Landan, da kasuwar dake dab da gadar, da kuma Vauxhall dake kudu maso yammacin birnin. A cewar bangaren 'yan sandan, an riga an tabbatar da cewa, lamuran biyu hari ne na ta'addanci, a yanzu haka 'yan sanda sun harbe mutanen uku da ake tuhumarsu da hannu a cikin lamuran har hahira.

Kafofin watsa labarun kasar Burtaniya sun ruwaito cewa wadanda suka ganewa idonsu faruwar lamarin sun ce, wata motar daukar kaya ta yi buge masu tafiya a gadar Landan, har ma an kai farmaki kan mutane da wuka, hakan ya rautata mutane da dama.
Bangaren 'yan sandan bai fayyace yadda aka kai farmaki a kasuwar dake dab da gadar London din ba. Amma, a cewarsu, lamarin kai farmaki da wuka da ya faru a Vauxhall ba shi da nasaba da sauran lamura biyu.

Za a shirya zabe a kasar Burtaniya a watan Agusta. Firaministar kasar Theresa May dake yakin neman zabe a sauran wurare ta riga ta komo fadarta cikin gaggawa a daren ranar Asabar din. (Bilkisu)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China