Fadar shugaban kasar Afrika ta Kudu, ta musanta zargin da ake cewa, Shugaba Jacob Zuma na da gida a Dubai, dake hadaddiyar Daular Larabawa.
Cikin wata sanarwa da ya fitar, kakakin fadar shugaban kasar Bongani Ngqulunga, ya ce labarin da jaridar Sunday Times ta wallafa, da ke cewa Zuma ya mallaki gida a Dubai karya ce.
Bongani Ngqulunga, ya ce shugaba Zuma, bai mallaki kaddara a wajen kasar ba, kuma bai nemi wani da ya saya masa wata kaddara a kasashen waje ba. (Fa'iza Mustapha)