in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tattalin arzikin Afrika ta Kudu ya dau matsayi na uku a nahiyar Afrika
2016-05-13 10:56:57 cri
Bisa rahoton hasashen tattalin arzikin duniya da asusun ba da lamuni na duniya IMF ya fidda, an ce, yawan kudin samar da kayayyaki da Afrika ta Kudu ta samu a shekarar 2015 ya kai matsayi na uku a Afrika, Masar ta zarce Afrika ta Kudu, ta zama kasar mai karfin tattalin arziki ta biyu a nahiyar.

IMF ya ce, dalilin da ya sa tattalin arzikin Afrika ta Kudu ya samu koma baya har zuwa matsayi na uku shi ne raguwar darajar kudin kasar wato Rand.

Sai dai a ganin wani jami'i na sashen kula da hadari na reshen Afirka ta Kudu na kamfanin ba da shawara game da hada-hadar kudi na duniya KPMG, ya ce, har zuwa yanzu, tattalin arzikin Afrika ta Kudu shi ne mafi kyau a nahiyar Afirka, sabo da tsarinsa ya shafi fannoni da sana'o'i daban daban.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China