in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika na bukatar inganta ayyunkan masana'antu don samun shiga a dama da ita a kasuwar duniya
2017-06-01 09:47:42 cri

Cibiyar tabbatar da sauyi a fannin tattalin arzikin Afrika dake Ghana ACET, ta bukaci kasashen Afrika su dauki matakan inganta ayyukan masana'antu, don shiga a dama da su a kasuwar duniya.

Cikin wata sanarwa da ta fitar jiya, gabanin taro kan sarrafa kayyayaki da za a yi cikin wannan watan a Addis Ababa, babban birnin Habasha, cibiyar ta ce nahiyar Afrika, ita ce koma baya cikin sauran nahiyoyin duniya wajen sarrafa kayyayaki, kuma a don haka, akwai bukatar inganta ayyukan masana'antu domin samun ci gaba ta fannin zaman takewa da tattalin arziki.

Sanawar ta ruwaito cibiyar na cewa, muddun nahiyar na son shiga a dama da ita a kasuwar duniya, sai ta magance wasu kalubale da ke dogaro da juna.

Cibiyar ta ce, duk da ci gaban da nahiyar ta samu a a shekarun 1960 zuwa tsakiyar 1980, a yanzu ta zama koma baya cikin sauran sassan duniya.

Taron wanda za a yi a ranar 5 ga watan nan, na da nufin kaddamar da tattaunawa kan yadda shugabannin kasashen Afrika za su inganta harkokin masana'antu kamar yadda yake cikin manufofinsu na kawo sauyi. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China