in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakiliyar Sin ta gabatar da fasahohin kiwon lafiya ta kasar a babban taron WHO
2017-05-23 10:55:59 cri
Jiya Litinin, a yayin babban taron kiwon lafiya na kasa da kasa karo na 70 da aka yi a birnin Geneva, shugabar tawagar wakilan gwamnatin kasar Sin, kana shugabar kwamitin kula da harkokin kiwon lafiya da shirin kayyade yawan haihuwa na kasar Li Bin, ta ba da jawabi inda ta bayyana cewa, gwamnatin kasar Sin za ta goyi bayan hukumar kiwon lafiya ta duniya ta WHO, wajen aiwatar da jadawalin neman dauwamammen ci gaba kafin shekarar 2030 ta fuskar ayyukan kiwon lafiya, kana kasar Sin tana son ba da gudummawa a wannan fanni yadda ya kamata.

Haka kuma, Ms. Li ta ce, gwamnatin kasar Sin tana mai da hankali kan kiyaye lafiyar al'ummar kasar a ko da yaushe, ta kuma mai da harkar kiwon lafiyar jama'ar kasar a matsayin abu mafi muhimmanci cikin shirin neman bunkasuwar kasar baki daya, shi ya sa, gwamnatin kasar Sin ta kafa wani shirin jinya bisa tushe dake tallafawa al'ummar kasar da yawansu ya kai mutane biliyan 1 da miliyan 300, inda ta kyautata yanayin adalci da kuma inganta aikin jinya, lamarin da ya dace da halin da kasar Sin take ciki, da kuma ba da tabbaci wajen cimma burin neman dauwamammen ci gaba nan da shekarar 2030.

A jiya Litinin ne, aka bude babban taron kiwon lafiya na kasa da kasa karo na 70 a birnin Geneva na kasar Switzerland, inda aka mai da takan taron "kafa shiri mai kyau wanda zai dace da kiyaye lafiyar mutanen kasa da kasa cikin lokaci na neman dauwamemmen ci gaba". (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China