in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta kara yawan taimako ga Syria a matsayin bangare na shawarar ziri daya hanya daya
2017-05-16 09:28:34 cri

Jakadan Sin a kasar Syria Qi Qianjin, ya ce kasar sa za ta kara yawan tallafin ta ga kasar Syria, a wani bangare na aiwatar da manufofin jin kai dake kunshe cikin shawarar ziri daya hanya daya.

Mr. Qi Qianjin ya bayyana hakan ne a jiya Litinin, yayin ganawar sa da shugaban sashen tsare tsare da hadin gwiwar kasa da kasa na Syria Imad Sabouni. Jami'an biyu sun kuma rattaba hannu kan takardun yarjejeniyar samar da tallafin abinci, da sauran kayayyakin jin kai don talllafawa al'ummar Syria.

Kaza lika da yake tsokaci game da burin gwamnatin Syria, Mr. Sabouni ya ce, babu abun da gwamnatin kasar mai ci ke maida hankali kan sa, sama da yunkurin wanzar da zaman lafiya, tare da tabbatar da cin moriyar juna tare da abokan huldar kasar, a fannonin samar da kayayyaki da na ba da hidima.

Ya ce, shawarar ziri daya hanya daya, na daya daga cikin muhimman tsare tsare dake tallafar tattalin arzikin kasar Sin da Syria tare.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China