in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen kasar Sin ya gana da takwararsa ta kasar Kenya
2017-05-15 10:51:44 cri
A jiya Lahadi, ministan harkokin wajen kasar Sin, mista Wang Yi, ya gana da takwararsa ta kasar Kenya, Amina Mohamed, wadda ke birnin Beijing na kasar Sin, domin halartar taron dandalin koli na hadin gwiwar kasa da kasa ta fuskar shawarar "ziri daya hanya daya".

Yayin ganawarsu, Wang Yi ya ce, jawabin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar wajen bikin budewar taron, ya shaida aniyar kasar Sin ta raya "ziri daya hanya daya" bisa manufar zaman lafiya, da neman samun walwala, da bude kofa, da kokarin kirkiro sabbin fasahohi. Hakan, a cewar ministan kasar Sin, ya tabbatar da hanyar da za a bi, wajen zurfafa hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka.

Ministan ya kara da cewa, Kenya wata muhimmiyar kasa ce a nahiyar Afirka, wadda kasar Sin ta fara da hadin gwiwa tare da ita a fannin raya masana'antu, don haka yana da imanin cewa, kasar Kenya za ta zama kan gaba tsakanin kasashen Afirka, a kokarin aiwatar da shawarar "ziri daya hanya daya".(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China