in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta fara daukar matakai game da bullar Ebola a DRC
2017-05-15 09:25:13 cri

Gwamnatin Najeriya ta bukaci 'yan kasar, da su kai rahoton duk wasu alamu na zazzabi mai sanya zubar jini, tare da fadakar da juna game da wannan cuta, domin kaucewa bullar cutar Ebola, wadda tuni aka tabbatar ta kama wasu mutane a janhuriyar dimokaradiyyar Congo DRC.

Cikin wata sanarwa da ministan lafiyar Najeriya Isaac Adewole ya fitar jiya a birnin Lagos, an ja hankulan cibiyoyin kiwon lafiyar kasar da su wayar da kan al'ummar kasar, tare da gabatar da rahoton bullar duk wata cuta dake iya zama babbar barazana ga mahukuntan kasar.

Mr. Adewole ya kara da cewa, hukumar lafiya ta duniya WHO, ta tabbatar da bullar cutar Ebola a janhuriyar dimokaradiyyar Congo, wanda hakan ya sanya gwamnatin Najeriya kafa cibiyoyin tantance mutane a kan iyakokin ta, domin sanya ido tare da dakile shigar wannan cuta ta Ebola mai saurin kisa.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China