in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mamakon ruwan sama zai iya habaka yabanya a gabashin Afrka
2017-05-14 12:26:49 cri
Wani rahoto game da samar da abinci da aka fitar a jiya Asabar ya nuna cewa, mamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka samu a karshen watan Afrilu da farkon watan Mayu zai iya samar da habakar amfanin gona a kasashen dake yankin gabashin Afrika.

A rahoton wata wata na shirin yaki da yunwa wato Early Warning Systems ko kuma (FEWS Net) a takaice, rahoton ya ce faduwar damina a kurarren lokaci na daga cikin matsotsolin dake haifar da gibi inda hakan ke haddasa fari a kasahen na gabashin Afrika.

Matsalar farin da aka fuskanta a kasashen gabashin Afrika a shekarar 2016, ya haddasa matsalar karancin abinci a kasashen da dama dake yankin na Afrika.

Amma wannan rahoto ya bayyana cewa, karuwar ruwan sama da aka samu a yan kwanakin nan ya inganta makomar amfanin gonar a kasashen Kenya, Uganda, Rwanda, Burundi, Demokaradiyyar Congo, da arewacin Tanzania.

Sai dai kuma, a wasu yankuna na kudanci Somalia da wasu sassa gonaki na kudu maso gabashin Kenya, rashin samun yabanya ya ta'allaka ne da rashin faduwar damina a kan lokaci shi ya sa ake samun matsalar rashin ingatattun amfanin gona. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China