in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Libya da kasashe makwabtanta sun ki amincewa da tsoma baki cikin harkokin kasar ta hanyar soja
2017-05-09 13:55:58 cri
Wakilan Libya da na kasashe makwabtanta sun bayyana cewa, ba za su amince da tsoma baki cikin harkokin kasar ta hanyar amfani da matakan soji ba.

Sun bayyana haka ne jiya Litinin, a wajen taron kasashe dake kewayen Libya karo na 11, wanda ya gudana a Algiers, fadar mulkin kasar Aljeriya.

Wakilan kasashe makwabtan kasar Libya mahalarta taron, sun nuna damuwa kan yadda wasu kasashen waje ke yunkurin daukar matakan soji a Libya, suna masu ganin cewa hakan zai lalata yanayin tsaron da yankin ke ciki.

Don haka suka bukaci a yi musayar ra'ayi tare da gwamnatin kasar Libya, kafin a dauki matakan soja cikin kasar don dakile 'yan ta'adda.

Ban da haka kuma, mahalarta taron sun bukaci bangarorin kasar Libya da su tsagaita bude wuta, tare da rungumar hanyar siyasa da shawarwari wajen daidaita rikicin kasar.

Haka zalika, an jaddada goyon baya ga jama'ar kasar Libya kan kokarinsu na samun masalaha tsakanin al'ummomi daban daban, da burin kafa hukumomi masu karfi a fannonin siyasa, aikin soji, da tsaro, don kare mulkin kasar da cikakken yankinta.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China