in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IS tana da karfin gaske a yankin Sirte dake kudancin kasar Libya
2017-03-28 16:23:25 cri
Mai magana da yawun rundunar sojin Libya dake samun goyon bayan MDD yace, duk da kokarin da dakarun gwamnatin ke yi na fatattakar mayakan kungiya mai da'awar kafa daular musulunci wato IS, har yanzu kungiyar tana da karfi a kudancin birnin Sirte.

Mohamed Gunono, shi ne kakakin rundunar kai dauki gaggawa ta jiragen sama, wadda MDD ke marawa baya, ya ce a halin da ake ciki a yanzu, dambarwar siyasa da kuma samun rarrabuwar kai ya haifar da mayakan na IS suna kara karfi

Gunono yace, bangarorin dake cigaba da takun saka ta fuskar siyasa a kasar basu yin la'akari da yanayin da kasar ta tsinci kanta. Yace bangarorin sun yi sakaci mayakan yan ta'daddan na kokarin yin amfani da rarrabuwar kawunan dake tsakaninsu.

Gwamnatin hadin kan kasar mai samun goyon bayan MDD ta bada sanarwa game da wani yunkuri da take yi na kafa wata rundunar tsaron mayaka 3,000 domin kwace ikon birnin na Sirte.

A ranar 15 ga wannan watan ne gwamnati ta bada sanarwa cewa har yanzu akwai mayakan na IS a yankin na Sirte, duk kuwa da galabar da dakarun gwamnatin suka samu wajen fatattakar yan ta'addan.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China