in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD za ta taimakawa Afrika samar da wata kafa ta cinikayya ta intanet
2017-05-09 11:08:11 cri
Hukumar gidan waya ta MDD UPU za ta taimakwa Afrika, wajen samar da wata kafa ta cinikayya ta intanet a nahiyar, domin bunkasa harkokin kasuwanci.

Darakta Janar na Hukumar UPU Bishar Hussein ya shaidawa wani taro kan harkokin sadarwa ta wayar tarho a Nairobi cewa, kafar da aka yi wa lakabi da Ecom@Africa, za ta samar da dimbin dammamakin kasuwanci ga 'Yan Afrika a duniya.

Ya ce sun lura cewa, an bar nahiyar Afrika a baya a fannin cinikayya ta intanet da ake yi a duniya, a don haka, kafar za ta ba nahiyar damar bin sahun sauran kasashen duniyar ta fuskar bunkasa harkokin cinikayya.

Hukumar ta zabi wasu kasashen da dama da take son fara shirin da su, da niyyar daga bisani, za ta hade su baki daya ta yadda za a samu cibiyar kasuwanci ta intanet a fadin nahiyar.

Kasashen da ta zaba sun hada da Kenya, da Afrika ta kudu, da Kamaru, da Cote d'ivoire, da Morocco, da kuma Tunisia. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China