in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'i: Najeriya zata saukaka hanyoyin cinikayya na kasashen ketare
2017-02-03 10:02:54 cri
Wani jami'i a Najeriya yace kasar zata hada gwiwa da cibiyar gudanar da kasuwanci da cinikayya ta hanyar na'urorin zamani ta MDD wato (UN/CEFACT), domin saukaka hanyoyin hada hadar kayayyaki zuwa kasashen waje.

Olusegun Awolowo, shine babban daraktan majalisar inganta harkokin fitar da hajoji zuwa ketare NEPC, ya shedawa manema labarai a Abuja, babban birnin kasar cewa, wannan mataki ya biyo bayan irin nasarorin da aka cimma ne a sha'anin saukaka hanyoyin kasuwanci da kuma rage lokacin da ake batawa wajen fitar da kayayyaki daga Najeriya zuwa kasashen waje.

Awolowo yace wannan na daga cikin yunkurin da hukumar NEPC take yi wajen samar da kyakkyawan yanayin kasuwanci ta hanyar saukaka hada hadar cinikayya ta cikin gida da kuma na kasa da kasa.

Yace Najeriya ta kasance kasa ta 107 a matsayin mamba a kungiyar kasuwanci ta kasashen duniya (WTO), inda ta rattaba hannu kan yarjejeniyar zama mambar a karkashin yarjejeniyar cinikayya ta (TFA) a birnin Davos.

Yace rahoton baya bayan nan da bankin duniya ya fitar ya nuna cewa Najeriyar ta samu cigaba kadan, inda ta tashi zuwa kasa ta 149 maimakon kasa ta 160 a baya cikin jerin kasashen duniya 190.

Mr. Awolowo, yace UN/CEFACT zata taka muhimmiyar rawa wajen amfanar da kananan 'yan kasuwa wajen saukaka fannin hada hadar kasuwanci da sauran batutuwa da suka shafi ciniki.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China