in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Al-Shabaab ta yi garkuwa da ma'aikatan bada agaji 4 a kudancin Somaliya
2017-04-05 09:42:04 cri
Ana zargin mayakan kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ta Al-Shabaab ta yi garkuwa da wasu jami'an hukumar lafiya ta duniya WHO su 4 a kudancin kasar Somaliya da safiyar ranar Talatar da ta gabata.

Wani jami'in dan sanda ya bayyana cewa dukkan jami'an 4, 'yan asalin kasar Somaliya ne, kuma suna aiki ne na rigakafin cutar polio a kasar ta Somaliya, karkashin shirin kiwon lafiya na MDD.

Jami'in, wanda bai amince a ambaci sunansa ba, ya tabbatar da cewa mayakan na A-Shabaab sun yi awon gaba da mutanen 4 ne a yankin Gedo a lokacin da suke yin bulaguro a kusa da garin Luuq.

Ya ce tuni aka fara tattaunawa domin cimma matsaya don a sako jami'an agajin su 4, inda wasu dattawa a yankin suke shiga tsakani domin a warware matsalar. Sai dai kawo yanzun babu wani karin haske daga hukumar ta WHO.

Kungiyar masu tsattsauran ra'ayin Islama ta Al-Shabaab mai fafutukar kifar da gwamnatin Somaliya mai samun goyon bayan kasashen yammaci, ba wannan ne karon farko da kungiyar ke kaddamar da hari kan jami'an ba da agaji na kasa da kasa ba, a lokutan baya ma, kungiyar ta sha yin garkuwa da jami'an domin neman kudaden fansa. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China