Da yake tabbatar da aukuwar lamarin, jami'in 'yan sandan yankin Ahmed Elmi, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, Bam din ya tarwatsa motar da yake ciki, a kusa da wani gidan cin abinci dake daura da ma'aikatar wasanni, da ta tsaron kasa dake kusa da juna, a gundumar Shangani dake birnin na Mogadishu.
Shi ma kakakin gwamnatin yankin Benadir Abdifitah Omar Halane, ya tabbatar da aukuwar harin, sai dai a cewar sa mutane 5 ne suka rasu. Halane ya ce jami'an tsaro na duba yadda al'amarin ya auku, da nufin damke wadanda ke da hannu a kitsa shi.
Kawo yanzu dai ba wata kungiya da ta dauki alhakin kaddamar da wannan hari. (Saminu)