in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya mika sakon ta'aziyya ga shugaban kasar Masar game da harin ta'addanci
2017-04-10 19:40:21 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aike da sakon jaje ga takwaran sa na Masar Abdel-Fattah al-Sisi, game da harin ta'addanci da aka kai kan wasu majami'u biyu a kasar ta Masar.

Cikin sako da shugaban na Sin ya gabatar a yau Litinin, ya bayyana matukar alheni bisa rasuwar mutane da dama, yana mai jajantawa shugaban na Masar, da iyalan wadanda suka rasa 'yan uwan su, da ma wadanda suka jikkata.

Shugaba Xi ya ce Sin na adawa da duk wani nau'in aiki na ta'adanci. Kuma kasar sa za ta goyi bayan Masar da al'ummar ta, wajen karfafa tsaron kasa, da wanzar da zaman lafiya, tare da yaki da daukacin ayyukan ta'adanci.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China