in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya yi Allah wadai da harin da aka kai majami'un Masar
2017-04-10 11:04:54 cri
Kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya ya fitar da wata sanarwa jiya Lahadi, inda ya yi kakkausar suka kan harin boma-bomai da aka kai wasu majami'u a biranen Tanta da Alexandria dake arewacin kasar Masar. Kwamitin sulhun ya jaddada cewa, ya zama dole a yanke hukunci mai tsanani kan wadanda suka kulla makarkashiyar kai harin, gami da wadanda suka ba da tallafi da wadanda suka kai harin. Ya kuma bukaci daukacin kasashen duniya da su ba da hadin-kai ga kasar Masar da sauran gwamnatocin kasashe a wannan fanni, bisa dokar kasa da kasa da ka'idojin MDD.

An kai wasu hare-haren bom kan majami'u a biranen Tanta da Alexandria dake arewacin kasar Masar a ranar 9 ga wata. Wata majiya daga ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar ta ce, hare-haren sun yi ajalin mutane a kalla 43, tare da raunata wasu sama da dari. Kungiyar IS ta sanar da daukar alhakin kai hare-haren.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China