Jam'iyya mai mulkin Afrika ta Kudu ANC, ta ce za ta gana da jama'iyyun kawance, domin tattaunawa kan kiran da ake yi wa shugaban kasar Jacob Zuma ya yi murabus.
Sakataren janar na jam'iyyar ANC Gwede Mantashe ne ya bayyana haka yayin da yake ganawa da manema labarai a jiya Laraba, game da taron kwamitin gudanarwar jami'iyyar NWC da aka yi ranar Talata.
Ko a ranar Litinin manyan jami'an jam'iyyar ANC sun gudanar da wani taro, domin nazari kan sauyin da shugaban ya yi a majalisar zartarwarsa a makon da ya gabata.
ANC dai na kawance ne da jami'yyar kwaminisanci na kasar SACP da kungiyoyin kwadago na COSATU.
Mantashe ya ce, kwamitin NWC ya jadadda bukatar ANC ta hada hannu da kawancenta domin amfanin kasar, inda ANC ta bi sahun kiraye-kirayen da SACP da COSATU da sauran jam'iyyu ke yi, dake neman shugaba Jacob Zuma ya yi murabus daga matsayinsa na shugaban jamhuriyar Afrika ta Kudu. (Fa'iza Mustapha)