in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kira da a inganta shirin ziri daya da hanya daya
2017-03-18 13:45:17 cri
Jiya Jumma'a, aka zartas da kuduri mai lamba 2344 kan batun Afghanistan a kwamitin sulhu na MDD, inda aka sa kaimi ga gamayyar kasa da kasa da su taimakawa kasar wajen raya tattalin arzikinta, yayin da karfafa hadin gwiwar kasashen dake yankin a fannin tattalin arziki bisa shirin tattalin arziki na zairi daya da hanya daya na karni na 21.

Haka zalika, an jaddada cewa, ya kamata a inganta hadin gwiwar sassa daban daban dake yankin domin tabbatar da zaman lafiya da ci gaban yankin, yayin da karfafa dunkulewar bil Adama.

Haka kuma, bayan an zartas da kudurin, zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Liu Jieyi, ya bayyana cewa, a watan Janairun bana, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi jawabi a hedkwatar MDD dake birnin Geneva, inda ya bayyana muhimmiyar ma'anar karfafa dunkulewar bil Adama, da kuma fidda dabarar Sin kan yadda za'a nemi cigaban kasa da kasa da wayewar kan bil Adama.

A wannan karo kuma, kwamitin sulhu na MDD ya zartas da kudurin mai lamba 2344, inda yake kunshe da manufar gina makomar bil Adama cikin hadin gwiwa, lamarin da ya nuna ra'ayi daya da gamayyar kasa da kasa suka cimma, da kuma babbar gudummawar da kasar Sin ta bayar wajen kyautata yanayin duniya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China