in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka tana kallon kasar Sin da tunaninta a harkokin kiyaye hakkin dan Adam, in ji kakakin kasar Sin
2017-03-06 20:10:15 cri

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya ce, tanade-tanaden da ke cikin rahoton kasashen duniya game da kare hakkin dan Adam na shekarar 2016, wanda ma'aikatar harkokin wajen kasar Amurka ta kaddamar a kwanan baya, ba su da kan gado, kuma Amurka tana kallon kasar Sin da tunaninta. Kasar Sin ta ki amincewa da rahoton, har ma ta tuntubi Amurkar a hukumance.

A yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing, Geng Shuang ya ce, har kullum kasar Sin na tsayawa kan yin tattaunawa da mu'amala a tsakanin kasa da kasa a harkokin da suka shafi kare hakkin dan Adam bisa ka'idar yin zaman daidai wa daida da girmama juna, a kokarin yin koyi da juna da samun ci gaba tare.

Geng Shuang ya ce, kasar Sin ta kalubalanci Amurka da ta rika kallon kasar Sin a fannin harkokin da suka shafi kare hakkin dan Adam bisa yadda abubuwa suka kasance a zahiri kuma cikin adalci, sannan ta daina fakewa da sunan kare hakkin dan Adam tana tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China