in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin da FAO sun hada gwiwa don taimakawa kasashe masu tasowa
2017-02-26 13:13:10 cri
Hukumar kula da batun samar da abinci da aikin gona ta MDD, wato FAO, ta bayyana a ranar Jumma'a da ta gabata cewa, hukumar da kasar Sin sun riga sun cimma matsaya, don karfafa hadin gwiwa da kasashe masu tasowa, ta yadda za a samu damar karfafa kwarewar kasashen a fannin raya kasa, da samun ci gaba mai dorewa.

Bisa wata yarjejeniyar da hukumar FAO da ma'aikatar aikin gona ta kasar Sin suka kulla a wancan rana, gwamnatin kasar Sin, za ta ware dalar Amurka miliyan 11, daga cikin kudin tallafi da take ba shirin hadin gwiwar kasashe masu tasowa na dala miliyan 80, don taimakawa wasu sabbin shirye-shirye 3 karkashin tsarin nan na hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa, ciki har da taimakawa kasashen aiwatar da yarjejeniyar kare itatuwa da bishiyu.

A cewarta, mataimakiyar sakataren janar ta hukumar FAO mai kula da batutuwan da suka shafi yanayi da albarkatun kasa, Madam Maria Helena Semedo, shirin raya hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa ya taka muhimmiyar rawa wajen mai da su zama masu cude-ni-in-cude-ka.

Jami'ar ta ce bisa kokarin bangarori daban-daban, musamman ma tallafin da kasar Sin ta bayar, an samu ci gaba sosai a wannan shiri, inda ta ce zai taimaka matuka, ta fuskar samar da isashen abinci a duniya, da tabbatar da samun ci gaba mai dorewa. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China