Shugaban kasar Somaliya Mohamed Abdullahi Mohamed ya bayyana sunan Hassan Ali Khaire, a matsayin sabon firaministan kasar sa.
Mr. Khaire, wanda ya yi aiki a matsayin jami'in shiyya, na hukumar lura da 'yan gudun hijira ta kasar Norway ko NRC a takaice, na da shaidar zama 'dan kasar Norway, baya ga kasar sa ta haihuwa wato Somaliya.(Saminu)