in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 30 sun rasu sakamakon harin boma-bomai a Somaliya
2017-02-20 10:22:34 cri

A jiya Lahadi 19 ga wata ne wani jami'in hukumar leken asiri, da kuma wani jami'in gwamnatin kasar Somaliya, suka tabbatar da aukuwar harin boma-boman da aka dasa cikin mota a wata kasuwa, wadda ke birnin Magadishu, fadar mulkin kasar Somaliya, lamarin da ya haddasa rasuwar mutane a kalla guda 30, yayin da wasu da dama suka jikkata.

Ya zuwa yanzu, babu wata kungiyar da ta sanar da daukar alhakin tashin bama baman. Ko da yake ana ganin cewa, reshen kungiyar Al-Qaeda dake kasar Somaliya watau kungiyar Al-shabaab, na yawan kaddamar da makamantan irin wadannan hare hare.

A ranar 8 ga wata, tsohon firaminista a gwamnatin wucin gadin kasar Mohamed Abdullahi Mohamed, ya lashe babban zaben shugaban kasar, inda kuma ake sa ran rantsar da shi a ranar 22 ga watan nan. A daya hannun kuma a 'yan kwanakin nan, kungiyar Al-Shabaab na kara matsa kaimi na kaddamar da hare-haren ta'addanci a kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China