in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan sanda a Kenya sun kama wasu mutane biyu da ake zargin 'yan kungiyar IS ne
2017-02-19 12:18:52 cri
'Yan sandan sashen yaki da ayyukan ta'addanci na kasar Kenya, sun kama wasu mutane biyu da ake zargin 'yan kungiyar IS ne a birnin Mombasa, yayin wani samame da suka kai da nufin kama matasa da suka shiga kungiyoyi masu tsatsauran ra'ayi na kasashen waje.

Majiyoyi daga rundunar 'yan sandan sun bayyana cewa, an dawo da mutanen da suka hada da namiji mai shekaru 20 da mace 'yar shekara 26 daga Turkiyya, inda suka sulale suka shiga kasar bayan sun karbi horo a Syria.

Kwamandan 'yan sandan Mombasa Peter Maelo, ya ce yanzu haka, ana yi wa mutanen tambayoyi don samun Karin haske game da ayyukan kunyar a Kenya.

Ya ce tun a watan Nuwamban da ya gabata aka fara bibiyar mutanen cikin sirri, bayan hukumomin Turkiyya sun shaidawa kasar Kenya alakarsu da kungiyar IS.

Ya kuma shaidawa manema labarai cewa, jami'an tsaro sun tsananta aikinsu a cikin Mombasa da sauran garuruwan dake gabar ruwa, da nufin dakile duk wani yunkuri na kai harin ta'addanci.( Faiza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China