in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Kamaru ya jinjinawa tawagar kwallon kafar kasarsa
2017-02-09 09:59:58 cri

Shugaban kasar Kamaru Paul Biya, ya jinjinawa kwazon da tawagar kwallon kafar kasarsa ta nuna, na lashe kofin gasar kwallon kafar nahiyar Afirka na bana wadda ta gudana a kasar Gabon.

Kamaru ta doke Masar a wasan karshe da suka buga ranar Lahadin karshen mako da ci 2 da 1, inda ta dauki kofin wannan gasa a karo na 5. Kafin hakan Kamaru ta dauki wannan kofi na nahiyar Afirka a shekarar 1984 a kasar kwadebuwa, da 1988 a Morocco, da shekarar 2000 a Najeriya, da kuma shekara ta 2002 a kasar Mali.

Kafin fara gasar dai ba a zata Kamaru za ta taka wata rawar gani ba, kasancewar a gasar shekarar 2015 wadda ta gudana a Equatorial Guinea, an cire ta tun a wasannin rukuni.

Da yake yabawa tawagar 'yan wasan da jami'an su, yayin wata liyafa da aka shirya a fadar gwamnatin kasar a jiya Laraba, shugaba Biya ya ce, kasarsa ta farfado a fannin kwallon kafa. Ya ce, shi da al'ummar kasarsa na matukar alfahari da nasarar kungiyar.

A watan Disambar bara ma dai shugaba Biya ya furta makamantan wadannan kalamai, lokacin da kungiyar kwallon kafar mata ta kasar ta zo na biyu a gasar nahiyar ajin mata karo na 10.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China