Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, zai ziyarci kasashen Australia da New Zealand, daga ranar 7 zuwa 10 ga watan nan, bisa gayyatar da takwarorinsa na kasashen 2 suka yi masa.
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, shi ne ya sanar da hakan a yau Jumma'a, a yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing. (Tasallah Yuan)