in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kama masu satar mai a Najeriya
2017-01-31 12:32:45 cri
Rundunar sojan ruwa ta Najeriya ta bayyana cewa, dakarunta sun yi nasarar damke wasu da ake zargin barayin mai a jihar Delta da ke yankin kudancin kasar.

Jami'in rundunar mai kula da yankin Mohammed Garba ya shaidawa manema labarai a garin Warri cewa, an lalata sansanonin tace mai ba bisa ka'ida ba 42, da tan 3,000 na danyen mai da aka sata da tan 1,000 da tataccen man gas a yayin wannan samame.

Jami'in ya kara da cewa, dakarun sun kuma yi nasarar kama wasu jiga-jigan batagarin da ke fasa bututan mai a yankin.

Rundunar sojojin ruwan dai ta lashi takwabin kawar da masu satar mai da sauran munanan ayyukan da ake aikatawa a kan teku.

Rahotanni na nuna cewa, satar mai ta durkusar da kudaden shigar da Najeriyar ta ke samu daga bangaren mai. (Ibrahim).

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China