in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar PENGASSAN a Najeriya ta yi kiran da a sanya dokar ta baci a bangaren man kasar
2015-06-16 10:38:11 cri
Kungiyar manyan ma'aikatan man petur da isakar gas a Najeriya (PENGASSAN) ta bukaci shugaban kasar Muhammadu Buhari da ya duba yiwuwar sanya dokar ta baci a bangaren man petur da iskar gas na kasar.

Shugaban kungiyar Emmanuel Onourah wanda ya bayyana hakan ga taron manema labarai a birni Lagos, cibiyar harkokin kasuwancin kasar ya ce, muddin majalisar dokokin kasar ba ta hanzarta sanya hannu kan dokar da ta shafi bangaren man kasar ba, hakan na iya barazana ga jarin da za a zuba a wannan bangaren daga sherkarar 2015 zuwa 2020 adadin ya kai kusan dala biliyan 80.

Shugaban kungiyar ya kara bayyana cewa,rashin sanya hannu kan wannan doka na iya rage yawan kudaden shigar da gwamnatin kasar ke samu a bangaren man da ya kai dala biliyan 44 cikin wannan lokaci.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China