in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO ta gargadi kasashe game da annobar murar tsuntsaye
2017-01-24 10:52:04 cri
Jiya Litinin, babbar daraktar hukumar lafiya ta duniya WHO madam Margaret Chan,ta yi kira ga kasashe daban-daban, da su mai da hankali wajen yaki da annobar murar tsuntsaye, tare da bada rahoto kan lokaci idan aka samu mutanen da suka kamu da cutar, ta yadda za a dakile yaduwar ta.

A wajen babban taron WHO karo na 140 da aka yi, Madam Margaret Chan ta yi nuni da cewa, tun daga watan Nuwamban bara, akwai kasashe da yankuna kusan 40 wadanda suka bada rahotannin cewa, sun gano annobar mura mai hadarin gaske tsakanin kaji da agwagin da ake kiwonsu a gida, gami da tsuntsayen daji, abun da ya sa hukumar WHO ta yi kira da a dauki matakan kare yaduwar annobar zuwa yankuna daban-daban.

Madam Margaret Chan ta kara da cewa, tun bayan barkewar annobar murar tsuntsaye mai nau'in H1N1 a shekara ta 2009 gami da 2010, kasashe suka daura damarar dakile yaduwar cutar a fadin duniya, sai dai ta ce, da sauran rina a kaba.

Chan ta jaddada cewa, bisa tanadin ka'idojin kiwon lafiya na duniya, idan aka gano dan Adam wanda ya kamu da cutar murar tsuntsaye, kamata ya yi a bada rahoto ba tare da bata lokaci ba, saboda 'rigakafi ya fi magani'.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China