in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A Nijeriya, za a fara tsaftace gonaki da sinadaran Chemical domin kare barkewar murar tsuntsaye
2017-01-14 12:48:50 cri
A kokarinta na kare yaduwar cutar murar tsuntsaye, Jihar Kano dake yankin arewa maso yammacin Nijeriya za ta fara tsaftace gidajen gona da kasuwanni da sinadaran kashe cututtuka..

Shehu Bawa, wanda shi ne Daraktan sashen kula da lafiyar dabbobi na ma'aikatar aikin gona dake jihar, ya shaidawa manema labarai a Kano cewa, tuni gwamnati ta amince da fitar da kudin sayan sinadaran.

Ya ce sashen na sa, ya kuma kara kaimi wajen sanya idanu a dukkan kasuwanni, domin tabbatar da ba a sayar da kajin da suka kamu da cutar ga jama'a.

Shehu Bawa ya kara da cewa, gwamnatin tarayya ta yi alkawarin biyan diyya ga wadanada aka samu barkewar cutar a gonakinsu tsakanin shekarun 2014 da 2015 da kuma 2015 zuwa 2016.

Sama da tsuntsaye dubu tara aka kashe a jihar, tun daga lokacin da aka samu barkewar cutar a ranar 15 ga watan Decemban da ya gabata. ( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China