in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Algeriya ta bukaci 'yan kasar Mali da su ci gaba da wanzar da zaman lafiya bayan harin ta'addanci
2017-01-19 09:37:26 cri

A jiya Laraba kasar Algeriya ta bukaci al'ummar kasar Mali da ba sa ga maciji da juna da su rungumi hanyoyin tabbatar da zaman lafiya a kasar, kana ta yi Allah wadai da harin kunar bakin wake da aka kaddamar a arewacin birnin Gao.

"Kasar Algeriya ta yi kakkausar suka game da harin ta'addancin da aka kaddamar a yau a birnin Gao", kamar yadda mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen Malin Abdelaziz Benali ya sanar wanda kamfanin dillancin labaran APS na kasar ya sanar.

Ya kara da cewa, Algeriya ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ci gaba da hada kai da mahukuntan kasar Mali da kasashen duniya, wajen daukar matakai da za su tabbatar da zaman lafiya a kasar ta Mali.

Dan kunar bakin waken ya yi yunkurin kaddamar da harin ne a sansanin sojojin kasar dake birnin Gao, lamarin da ya yi sanadiyyar hallaka mutane 50, da kuma jikkata mutane 60.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China