in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Masar sun ratabba hannu kan yarjejeniyar fahimta juna kan fasahar zamani da muhalli
2017-01-17 10:39:34 cri

A jiya Litinin ne kasashen Sin da Masar suka rattaba hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna, da za ta bunkasa ayyukan fasahar zamani, da cinikayya, da raya masana'antu a tsakaninsu.

Sakatare janar na kwamitin raya kasa da kwaskwarima na kasar Sin Li Pumin ne ya rattaba hannu a madadin kasar, yayin da ministan harkokin sadarwa da fasahar zamani na kasar Masar, Yaseer Qadi ya rattaba hannu a madadin kasarsa.

Yarjejeniyar na da nufin samar da wani rumbun adana bayanai domin huldar cinikayya da zuba jari ta intanet, tare da karfafa hadin gwiwa a fannin fasahar zamani, ta hanyar amfani da wani sabon tsari mai suna 'Online Silk Road' da zai hada biranen kasar Masar da takwarorinsu na kasar Sin.

Har ila yau, a jiyan, Li Pumin tare da jami'an ma'aikatar kare muhalli ta Masar, sun rattaba hannu kan yarjejeniyar kara bunkasa dangantakar kasashen, kan batutuwa da suka jibanci muhalli.( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China