Sojojin kasar Masar sun kashe 'yan ta'adda 22 a arewacin Sinai a ranar Alhamis, in ji kakakin rundunar sojojin kasar. Samamen ta sama da sojojin suka kai ya kuma lalata wani sansani inda 'yan ta'adda ke taruwa a kauyen Al-Laftat na Cheikh Zuwaid, da ke arewacin Sinai.
Ana samun gumurzu ko da yaushe tsakanin sojojin Masar da 'yan ta'adda a yankin Sinai tun lokacin da sojoji suka hambarar shugaba Mohamed Morsi a shekarar 2013. (Maman Ada)