in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tabbatar da harin kunar bakin wake da aka kai yankin arewa maso gabashin Nijeriya
2017-01-10 09:21:35 cri

A jiya Litinin ne, rundunar 'yan sandan jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya, ta tabbatar da aukuwar hare-haren kunar bakin wake uku a Maiduguri, babban birnin jihar, da kuma wani tsohon sansanin mayakan kungiyar Boko Haram.

Kakakin rundunar 'yan sandan jihar Victor Esuku, ya ce hare-haren da aka kai ranar Lahadi, sun yi sanadiyyar mutuwar wasu fararen hula biyu da wani dan banga.

Victor Esuku ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na kasar Sin wato Xinhua cewa, 'yan kunar bakin waken sun yi kokarin shiga cikin birnin Maiduguri ta yankunan Garki Muna da Kaleri dake jihar.

Ya ce, 'yan kunar bakin wake maza guda uku, sun tarwatsa kansu a kusa da shingen binciken soji dake Garki Muna, yayin da biyu mata kuma suka rasa rayukansu a Kaleri.

A watan da ya gabata ne, jami'an tsaron Nijeriya dake yankin arewa maso gabashin kasar, suka kai farmaki kan 'yayan kungiyar Boko Haram, inda suka fatattake su daga dajin Sambisa. ( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China