A sakonsa, Li Keqiang, ya jimanta mutuwar mutanen da harin ya rutsa da su, inda ya jajantawa Firaministan da kuma iyalansu, da kuma wadanda suka jikkata.
Da sanyin safiyar ranar Lahadi ne, wani dan bindiga dadi ya kutsa gidan rawa na Reina dake Istanbul, inda ya yi harbin kan mai uwa da wabi, kan daruruwan mutanen da suka taru don bikin shiga sabuwar shekara, al'amarin da ya yi sanadin mutuwar mutane talatin da tara,yayin da wasu sama da sittin suka jikkata.
Gwamnan Istanbul Vasip Sahin ya bayyana harin a matsayin na ta'addanci. (Fa'iza Mustapha)