in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Sin na adawa da duk wata mu'amala a hukumance tsakanin Amurka da Taiwan
2016-12-28 14:06:23 cri
Yau Laraba 28 ga wata ne mai magana da yawun ofishin kula da harkokin Taiwan, na majalisar gudanarwar kasar Sin An Fengshan, ya shaidawa 'yan jaridu cewa, harkar Taiwan na shafar ikon mulki, gami da cikakken yankin kasar Sin, kana aba ce mafi muhimmanci da jawo hankalin jama'a ta fuskar alakar kasashen Sin da Amurka.

Ya ce Sin na kan bakan ta na kin amincewa da Amurka ta yi duk wata mu'amala a hukumance, ko alaka ta soji kai tsaye da Taiwan, haka kuma ba za ta amince Amurkar ta sayar da makamai ga Taiwan ba. Wannan babban matsayi ne da gwamnatin kasar Sin ke tsayawa a kai, wanda sam ba za ta canja shi ba.

Mista An ya kuma bayyana cewa, kasar Sin na fatan Amurka zata mutunta manufar kasar Sin daya tak a duniya, da hadaddiyar sanarwa uku da aka daddale tsakanin Sin da Amurka. An ya ce, ya zama dole Amurka ta yi taka-tsantsan game da batutuwan da suka shafi Taiwan. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China