in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta ki amincewa da huldar da aka kulla tsakanin Amurka da Taiwan
2016-12-10 12:59:42 cri
Mista Lu Kang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, ya furta a jiya Jumma'a cewa, kasar Sin ta ki amincewa da mu'amala bisa matsayin jami'an gwamnati ko kuma a fannin aikin soja tsakanin kasar Amurka da yankin Taiwa, kuma ba ta son ganin kasar Amurka ta sayar da makamai ga Taiwan. Hakan, a cewar jami'in, ya kasance manufar kasar Sin da take tsayawa a kai, wadda kasashen duniya suka santa sosai kan wannan manufa.

Kafin haka, majalisar dokokin Amurka ta zartas da wata dokar da ta shafi aikin tsaron kasar, wadda a cikinta aka bayyana yunkurin karfafa mu'amalar jami'an Amurka da na Taiwan ta fuskar aikin soja. Dangane da wannan lamari, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya ce, batun Taiwan ya shafi ikon mulkin kasa da cikakken yankin kasar Sin ne, don haka yana da muhimmanci matuka.

Jami'in ya kara da cewa, tun lokacin da majalisar dokokin Amurka ta fara tattaunawa kan kudurin dokar, kasar Sin ta sha nuna kin amincewarta a lokuta da dama kan wannan batu. Yanzu kasar Sin tana kalubalantar kasar Amurka da ta tsaya kan iya yarjejeniyoyin da ta kulla da kasar Sin, sa'an nan ta yi taka-tsantsan wajen tsoma baki kan batun Taiwan. Bai kamata ba a haifar da matsala ga al'amuran siyasar duniya, da raunata huldar dake tsakanin Sin da Amurka, in ji jami'in na kasar Sin.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China