Jami'ai daga hukumar kashe gobara gami da kungiyar shawo kan annoba ta kasar Ghana, sun bayyana jiya Alhamis cewa, wani abu da ya fashe a wani gidan mai dake babbar cibiyar baje-koli ta kasa da kasa dake Accra, babban birnin kasar Ghana a daren jiya, ya yi sanadin mutuwar mutane a kalla 7, tare da raunata wasu 12.
Wasu ganau ba jiyau ba, sun ce bayan fashewar, wuta ta ruru har zuwa ginin babbar cibiyar baja-koli ta kasa da kasa.
Sai dai 'yan kwana-kwana sun kai dauki, inda suka shawo kan gobarar.
Har yanzu dai, ana ci gaba da binciken musabbabin gobarar.(Murtala Zhang)