in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana za ta watsa yadda ake tattara sakamakon zaben kasar kai tsaye a Disamba
2016-11-11 09:14:12 cri

A karon farko, kasar Ghana ta ba da damar girke na'urorin talabijin a cibiyoyin tattara sakamakon zaben kasar da za'a gudanar a watan Disamba domin a kalli yadda ake tattara sakamakon zaben kai tsaye ta gidaden talabijin din kasar.

Kafafen yada labaran kasar sun jiyo shugabar hukumar zaben kasar Charlotte Osei, tana bayyana hakan a jiya Alhamis.

Osei, wacce ta bayyana hakan a wani taron dandalin editoci da aka gudanar a Accra, ta ce wannan mataki zai ba da damar samun zabe mai inganci a zabukan shugaban kasa, da na majalisar dokokin kasar da za'a gudanar a ranar 7 ga watan Disamba.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China