in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Kenya ya bukaci huldar kasuwanci da kasashen kudu maso kudanci
2016-11-26 13:16:22 cri
Shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta, ya bukaci karfafa dangantakar kasuwanci tsakanin kasarsa da kasashen Latin Amurka da na yankin Caribbean.

Cikin wata sanarwar da aka rabawa manema labarai a Nairobi, Kenyatta, ya ce ta hanyar huldar kasuwanci ne al'ummomin kasashen dake yankin kudu maso kudanci za su ci moriya.

Shugaban na Kenya ya yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta ba da dukkannin goyon bayan da ake bukata domin bunkasa dangantakar kasuwanci tsakanin kasashen yankunan kudu maso kudanci.

Tawagar wakilan kasashen ta ziyarci kasar Kenya ne a karon farko, domin halartar taron koli na huldar kasuwanci tsakanin kasashen Latin Amurka da na Caribbean da kuma Afrika wanda ke gudana a birnin Nairobi. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China