in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a ingiza yunkurin siyasa a Sudan ta Kudu
2016-11-18 19:00:43 cri
Mataimakin zaunannen wakilin Sin dake MDD Wu Haitao ya bayyana a jiya Alhamis 17 ga wata cewa, kamata ya yi kasa da kasa su gaggauta ingiza bangarori daban daban na kasar Sudan Kudu, da su koma teburin shawarwari ta hanyar siyasa, su kuma aiwatar da yarjejeniyar shimfida zaman lafiya, da warware kalubalen da ake fuskanta a kasar ta hanyar tattaunawa.

Kwamitin sulhun MDD ya gudanar da wani taro a wannan rana, inda aka tattauna kan batun kasar Sudan ta Kudu. A gun taron, Wu Haitao ya bayyana cewa, Sin na goyon bayan jama'ar Afirka game da warware matsalolin nahiyar, da nuna goyon baya ga kungiyar shugabannin gabashin Afirka a kokarin ta na taka muhimmiyar rawa kan warware matsalar kasar Sudan ta Kudu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China