in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yan tawayen Sudan ta kudu sun bukaci Kenya ta saki mai magana da yawun kungiyar wanda ake tsare da shi
2016-11-04 10:25:50 cri
Jamiyyar adawa ta SPLM-IO a Sudan ta kudu, wadda hambararren mataimakin shugaban kasar Riek Machar ke jagoranta, ta bukaci kasar Kenya da ta sako jami'inta, wanda take zargin ana tsare da shi a filin jirgin saman kasar dake Nairobi.

Mataimakin mai magana da yawun SPLM-IO, Major Dickson Gatluak, ya ce James Gatdek Dak, shi ne mai magana da yawun Machar, ana tsare da shi a halin yanzu, kuma akwai yiwuwar za'a tisa keyarsa zuwa Sudan ta kudu.

Bacewar Dak, ta zo ne bayan da sakatare janar na MDD Ban Ki-moon, ya ba da sanarwa a ranar Talata na korar laftanal janar Johnson Kimani Ondieki dan asalin kasar Kenya, daga mukamin kwamandan rundunar wanzar da zaman lafiya ta MDD a Sudan ta kudu.

Wani rahoton MDD ya ce, mista Ondieki, ya ki maida martani game da harin da sojojin gwamnati suka kaddamar a harabar bada agaji dake Juba babban birnin Sudan ta kudu, a lokacin wata arangama tsakanin dakarun gwamnati da na yan tawaye a watan Yuli. Kuma a lokacin harin ne aka yiwa wasu mata jami'an aikin bada agaji fyade.

Shi dai Dak, ya yi na'am da korar da aka yiwa Ondieki, matakin da ake zargin shi ne ya harzuka gwamnatin Kenyan.

Kasar Kenya, ta ayyana cewar sallamar da aka yi wa jami'in ya fusata ta, kuma hakan ya sa ta yanke shawarar janye dakarunta daga Sudan ta kudu. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China