in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kenya za ta bunkasa masana'antun kasar domin cike gibi
2016-11-17 09:26:45 cri

Wani kusa a gwamnatin kasar Kenya ya bayyana cewa, kasar za ta mai da hankali wajen bunkasa masana'antu domin cike gibi a fannin hada hadar kasuwancin.

Ministan ciniki da masana'antu da hadin gwiwa na kasar Adan Mohammad, ya shedawa 'yan jaridu a Nairobi cewa, a halin yanzu, adadin kayayyakin da kasar ke shigowa da su daga kasashen ketare ya ninka har sau uku idan aka kwatanta da wanda take fitarwa zuwa kasashen waje.

Muhammad ya kara da cewa, bunkasa ci gaban masana'antu zai taimakawa kasar Kenyan wajen rage gibi ta fuskar takaita shigo da kayayyaki daga kasashen ketare.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China