Helkwatar tsaron Najeriya ta musanta rahotannin dake cewa, an dauko hayar sojoji daga kasashen waje domin amfani da su wajen yaki da Boko Haram.
Wasu kafafen yada labarai na cikin gida sun rawaito cewa, an dauko hayar wasu sojoji daga ketare domin ci gaba da yakin da dakarun kasar ke yi da mayakan Boko Haram.
Da yake mai da martani game da rahoton, mai magana da yawun helkwatar tsaron Najeriyar Rabe Abubakar, ya shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, wannan rahoto karya ce tsagwaronta, kuma babu kamshin gaskiya kan rahoton. Ya ce, dakarun Najeriya suna da karfi, da kuma kwarewar da za su iya rusa duk wata maboyar 'yan ta'adda dake fadin kasar.(Ahmad Fagam)