in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta nemi 'yan Boko Haram su mika wuya bayan barin wuta a maboyar mayakan
2016-10-13 10:11:13 cri

A jiya Laraba gwamnatin Najeriya ta bude kofa ga mayakan kungiyar Boko Haram wadanda ke da muradin ajiye makamansu, bayan da dakarun Najeriyar suka yi barin wuta a maboyar mayakan dake dajin Sambisa a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar.

Kwamandan rundunar sojin saman kasar Sadiq Abubakar ya bayyana cewar, sojojin saman Najeriyar suna ta kokarin murkushe 'yan ta'addan domin tabbatar da zaman lafiya a arewa maso gabashin kasar.

Bugu da kari, dakarun Najeriyar sun hallaka mayakan Boko Haram 2 a lokacin wani simame da suka kaddamar a kauyukan Ladin Buta da Juwano dake yankin Jere a jihar Borno.

Kakakin rundunar sojin kasar kanal Sani Usman, ya ce, sojojin kasar na ci gaba da farautar 'yan ta'addan, wadanda ke addabar jama'a da kaddamar da hare hare kan mazauna yankunan tare da hallaka jama'a, da yin garkuwa da mutane da kuma yin fashi da makami a yankunan.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China