in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya za ta kara adadin kamfanonin sarrafa shinkafa
2016-11-11 09:43:02 cri

Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa, za ta kara adadin kamfanonin sarrafa shinkafa domin cimma burin da kasar ke da shi na samar da shinkafa a cikin gidan nan da shekarar 2018.

Ministan noma da raya karkara na Najeriyar Audu Ogbeh, ya tabbatar da hakan ga 'yan jaridu a Abuja cewa, tuni gwamnatin kasar ta fara shirye shiryen samar da karin kamfanonin sarrafa shinkafa guda 40 domin cimma wannan buri.

A cewar Ogbeh, manufar shirin Najeriyar na inganta kamfanonin sarrafa shinkafa ita ce, domin samar da kasuwanni na cikin gidan da kasashen ketare ga manoman kasar, da kuma ba da karin damammaki domin habaka harkar noma a kasar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China