in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar 'yan majalisun Afrika na mai da hankali kan yaki da ta'addanci da ci gaba mai karko a Afrika
2016-11-09 10:56:24 cri

Kalubalolin ci gaba mai karko a Afrika da yaki da ta'addanci sun kasance manyan batutuwa na ayyukan zaman taron shugabannin majalisun dokoki na kungiyar 'yan majalisun Afrika (UPA) karo na 39 da aka bude a ranar Talata a cibiyar zauren masharwata wato zaure na biyu na majalisar dokokin Morocco dake birnin Rabat.

Mahalarta a wannan haduwa za su mai da hankali kan halartar 'yan kasa, musammun ma matasa kan bunkasa tsarin demokaradiya da yaki da ta'addanci a Afrika, in ji Abdelhakim Benchamach, shugaban zauren mashawarta a gaban 'yan jarida.

Haka zalika, mahalartan za su tattauna rawar da 'yan majalisun dokokin Afrika za su taka wajen tabbatar da muradun ci gaba mai dorewa, ta yadda za a fadada muryar Afrika game da wannan batu, da kuma fitar da wani tsinkaye na hadin gwiwa kan wannan batu, da ya kamata a gabatar a yayin taron COP22 a Marrakech, in ji mista Benchamach. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China