Dole ne kasashen Afrika su tanadi matakai da karfafa sanya ido kan iyakokinsu domin hana kungiyoyin ta'addanci da ke nahiyar samun makaman kare dangi.
Wannan kira, an yi shi ne a yayin wani dandali da aka bude a ranar Litinin a birnin Nairobi na kasar Kenya, wanda ya samu halartar kwararru a fannin tsaro, diplomasiyya da kuma masu fada a ji. Kungiyar tarayyar Afrika (AU) ta shirya wannan dandali tare da taimakon kungiyar ci gaban kasashen IGAD, da cibiyar nazarin harkokin tsaro ta kungiyar tarayyar Turai (EU) wato ISS. (Maman Ada)